
Episode #14
Fatawowin Rahama: Q&A 9-8-2026 - Prof. Sani R/Lemo
*Fatawoyin Rahma* Ranar Lahadi 25/2/1448 - 9/8/2026 Tambayoyi da Amsoshi tare da *Prof. Muhammad Sani Umar R/Lemo, OON* 1. Hukuncin Dillanci! 2. Mutumin da yake so wata, ita ma take sonsa, amma iyayensa ba sa son su tare; yaya zai yi? 3. Hukuncin wanda ya ci abinci yana azumi da mantuwa! 4. Hukuncin yin kyauta ga ma’akacin Immigration da yayi aikin yin passport ga mutumin da ya masa kyauta! 5. Hukuncin rage shekaru don a daɗe a na aiki? 6. Hukuncin kiwon dabbobi domin siyarwa Kiristoci lokacin bukkunansu! 7. Ya hallata mutum ya bibiyi ma’aikatu domin bankaɗo cin hancin da rashawa? 8. Hukuncin ta da iƙama bayan Kiran sallah-ba tare da tazara ba. 9. Yaya hukuncin tube mace tumbur a mata tiyata! 10. Hukuncin yara da ba sa turawa mahaifinsu kuɗi saboda ya na da kuɗi kuma mahaifiyar su ta umurce su da ka da su ta ra masa! 11. Ta yaya mutum zai bambance jarabawar da Allah ya masa saboda laifinsa da kuma jarabawar da Allah ya yi masa domin daukakar darajarsa! 12. Dole ne mutum ya san ma’anar adduar da ya ke yi? 13. Yaya ake yin Istikhara? 14. Za a yi salatin Annabi ﷺ a sallar nafila? 15. Wanda ya mutu ta hanyar nitsewa a ruwa ko gobara, za a masa wanka? 16. Shawara ga mai fama da matsanancin wasuwasi? 17. Hukuncin wanda yayi ƙarya akan halayyar wani mutum! 18. Yaushe ake “ as-sallatu khairul minannaum”? 19. Falalar Limanci? 20. Ana yin azumin kaffara ga wanda ba musulmi ba? 21. Hukuncin Jami’an tsaron da suke hana wanda aka tsare yin sallah!





